Dare Dubu Da Daya

0

Musulunci  da  musulmai  su suka kawo duk wani  cigaba a komai na duniya,kowane fanni ka fara bincikensa na tarihin kawo shi. Da kuma cigabansa a duniya zaka ga cewa Musulmai sun taka wata irin rawa wadda  ba wanda ya taka kamarta a duniya.

Zaka ga nasu sunyi shi cikin tsafta  da ilmi da kuma  basira da  hikima amma aka dauki nasu aka  gyara ko aka yi ma illa koma  aka bata shi ko kuma aka  ingantashi aka maida  shi hankaka maida dan wani naka.ma ana wadanda suka  sata daga musulunci su yi  karyar cewasune ahlin  abin.

Duk  wani  cigaban duniya  ya samo asali ne daga  adabi,watau rubuta littafi, wanda ,marubuta kanyi  don su fito da wani ilmi ko suyi wani hannunka maisanda  ko  kuma  suyi  wata  nusarwa.Rubutu ne farko sai a maida shi wani tabbatacen aikin ilmi.

Daya daga  cikin littafin da Abu  da  uwargidansa suka aiko mani daga  Landan akwai littafin  nan  Mai suna DARE DUBU DA DAYA.fassarar turanci wanda keda sifili uku. Kowane sifili yana da  shafi   dari  tara da Hamsin.950.KUma   rubutun kana na ne. so sai.

Wannan littafin shine  wanda ba littafin  dab a taba kamarsa  ba a tarihin adabin hikaya.a duniya.shine littafin da yai tasiri gaduk  marubutan  hikaya na duniya kuma  har yanzu ana kwafa  daga gareshi har yanzu ba   kureshi   ba.Anyi fina finai dayawa  daga  labaran littafin.

Ba  wani yare  Babba a duniya  da  ba fassara  wani bangare na littafin  a Harshen yaren ba.ko kuma  aka kwaikwayi salon littafin aka yi wani littafin da wannan yaren.Misali  salon da kuma labaran littafin  aka dauka aka  rubuta littafin MAGANA JARI CE TA DAYA  ZUWA TA UKU.wadda marigayi  Abubakar  imam ya rubuta.

Haka kuma tun zamanin turawa  an fara  fassara littafin da  Hausa, wanda  wani bature ya fara  har   rubutun ya kai  dare  n a dari  da hamsin  sai   ya tsaya. Kamfanin  Gaskiya   co orparation dake  zaria.ya yi aikin buga littafin  sai dai  shi  a  littafin  farko  dan biyu, Hausar  bata  karantuwa.  Sai  daga littafi na uku ne, littafin  ya  fara   zaka iya karantwa  ka  gane  sunansa   DARE   DUBU DA DAYA. An buga   shi daga  littafi na daya  zuwa  na  biyar  aka tsaya.Ana   samunsa  Har yanzu a  kasuwa,

Rubutun  bana yi shi bane  a matsayin wata  takardar  d azan gabatar  don,ilmim   adabi. Dana kawo marubutan kasashe da suka  shahara a kasashensu amma bisa dogara da   kwaikwayon da  kuma dauko labarai  daga littafin Dare dubu daya suna sarrafa  shi.A  kasashen asiya  turai da amurka.gabas ta  tsakiya  da kuma  afrika.

Farfesa   Ibrahim  Malumfashi malami   a jami ar   usman dan fodiyo dake sokoto.shine shaihin malamin daya  goge  akan sanin  tarihin wannnan littafin da kuma   yadda  aka  rubuta   shi.Malamin  masani ne so sai  akan  salon adabin wannan littafin da kuma tasirinshi a duniya.ya  rubuta takardu  na ilmin adabi  masu yawa  akan wannan. Ya kuma yi  littafi. Akan  Rubutu da rayuwar   Abubakar  imam. Wanda a cikin  ya kawo yadda littafin Dare dubu da daya  yayi ma imam tasiri,da kuma  tasiri ga  rubuce  rubucensa.

Dare dubu  da daya shine tasirin  da yayi ma kasar  Hausa  da kuma AFrikawa  wanda ta jawo  aka san kasar  da yin tatsuniya da  dare. Wanda  ada uwaye kanyi  ma  ya ya don  a hana su fita  suje yawo  a waje ko kuma a tsuniyar a  kawo wasu   hikima mai tasiri wanda  zata  kawo ma yaro wani darasin rayuwa.

Wani  abu da  littafin dare  da  daya shine ba wanda  yasan waya rubuta shi.ko kuma  suwa suka  rubuta  shi.wani  abu ne wanda har yanzu ake muhawarashi a duniyar adabi  da kuma ilmin tarihin littafin.wasu  sunce mutum  daya ne  da iyalashi  su kayi  aikin  wasu suka ce a a agungun  mutane suka yi aikin,

Hatta tsawo lokacin da aka  dauka   ana aikin littafin ana   muhawara  akanshi.wasu sunce lokaci guda akayi  aikin wasu kuma  sunce  a a tsawon lokaci aka  dauka  wasu sukayi  suka tsaya  a wani  wuri wasu  kuma suka dasa    da haka  aka  samu littafin.

Amma  abin  da aka samu tabbaci akayi  duk wanda ko wadanda suka  rubuta littafin malamai ne masana  addinin musulunci.domin  yadda a littafin  ake gwada  tsananin   fahimta na addinin musulunci.wasu kuma suna  da muhawarar cewa wanda yayi rubutun wani sufi  ko kuma  sufaye  ne. saboda  yadda ake  yawan nuna  girman  Allah acikin littafin.An fara littafin ne da  basmala.da salati

Akwai  ma masu  muhawarar  cewa  marubutan ko marubucin  dan  a kidar   shi a ne.saboda yadda  a rubutun littafin  ake tona yadda  sarakuna dake    rayuwa wancan lokacin ke rayuwa. Kuma  suna kiran kansu  sarakunan musulunci.irin tabargazar  da suke  da kuma aika aika.wannnan yasa  masu wannan ra ayi   sukace    marubutan shi a ne  don su nunama yana baya   abin day a faru a wani  salon rubutun koda  kuwa   an danne  bullar littafan tarihi.da kuma yadda a duk labaran dake cikin littafin zaka ga akwai   girmama  sunaye  irinsu  Fatima. Hassan, Husaini  da sauran  sunaye wadanda malaman  shi a ke  girmamawa.

Ana tsammanin an rubuta littafin ne. a  zamanin mulkin sarkin dake kira na musulunci  Haruna  Rashid.wasu kuma sun ce bayan shi. Wasu  kuma sunce  an fara rubuta  shit un zamanin  Haruna   Rashid, rubutun ya  dau tsawon lokaci  har  zuwa  wajen  sarakunan MUsulncin  zamanin  guda hudu ko biyar.wannan yasa  ake ganin tabbacin cewa rubutun gadonshi  aka rika yi.wasu ko wani yatsaya  a wani wuri  wasu kuma suka dasa  Su ka cigaba , tayiyu kamar  yadda  akayi  masu   wasiyya.

Asalin littafin an   rubuta shi ne da larabci  da  sunan ALFUN LAILA  WA LAILA.Ma ana  dare   dubu  da  daya. Faefesa  Malumfashi. Ya  rubuta  a littafinsa dabin Abubakar  Imam. Cewa  akwai muhawarar cewa  asalin littafin na Alfun Laila wa laila.da farisanci  aka rubuta shi  fassarashi  akayi zuw larabci. Na  larabcin ne  ya  shahara. Ya danne. Na farisanci.harma ya badda shi a tarihi.

Bugun tarihin  larabci  da ake dashi.an nuna an fassaro shi ne daga wani yare.wanda  yana yi labaran dake ciki aka  gane  daga  farinsanci ne.da  kuma irm wakokin da marubucin ya rika kawowa.ittafin  bugun  farko   yana da  sifili goma   sha biyu.amma  an rika  tace shi  don ya  zama  karami  dai  dai  samuwar  kowa  har  akayi wani sifili  biyar waani uku,

Littafin ya cika  duk wata kaida ta adabi. Salon labari .dadin  labari  wasa da harshe da kuma hasashe da hannunka mai sanda  da ban tsoro da wa azi ban tausayi  ban takaici. Da jin haushi.waka  was an kwaikwayo. Da kuma rike  mai karatu yaji in ya fara  sai ya kamala.har yanzu ba ai littafin tatsuniya  da aka zuba  hikima kamarsa ba.kuma babu wata Nahiya a  duniya  da mai littafin bai  tabo ba awani yanayin laarinsa.

Wani lokaci kuma akan  rika   rairaye   labara nana  littafai   dasu  aba littafan suna  daban daban  ana rubuta cewa ana dauko ne daga littafin dare dubu da daya.da haka  littafin da labaransa   ya watsu ba tare   wani  ya taba gani hakikanin littafin ba.

Fassarar  turanci  ta littafin kamar  yadda  farfesa  Malumfashi ya  shaida mani.  Akwai mai  sifili goma sha  biyu  shima.karamin  shine mai sifili biyu, wanda an tace an kuma tsamo  muhimman labaran acikin  sifili biyu. Kawai, Amma    a turanci anyi  dinbim littafai  da labaran  littafin.

A   india da  kasar  chaina nan ne   akayi ma littafin wani irin fassara  domin sunce  wasu  labaran littafin  sunyi kama  da  al adunsu na hindu  da buddah nan ne  suke  da  cikakken  fassarar littafin mai  sifili   ar ba in,da  dimbin littafai  da fina fina daga littafin.Farfesa  Malumfashi  yace  mani  a tarihin duniyar  adabi ba wani littafin  da yayi tasiri a duniya kamar dare dubu  da daya.littafin ya taimaka wajen  bincike da fahimtar musulunci, a yankin, harda  wasu   wuraren,na   asiya  da turai.

See also  HAUSA BA DABO BA

Don  ba yadda  zaka  karanta  littafin ka tsallake koyarwa  musulunci  da sakonsa.saboda  a rubutun  an girmamama   sakon  da musulunci  yazo  dashi.wannan yasa  wani manazarcin littafin wanda ba musulmi bay a rubuta  cewa  yana da  wuya ga wanda  ba  musulmi ba. Ya gama  nazarin littafin. Bai koma yayi   nazarin addinin musulunci  ba.

Littafin  ya ginu ne  bisa labarai na almara da   ta tsuniyi  masu  hikima  da koyar da darasi  da  kuma jan hankali da dadin gaske.wasu  kuma  misalan  labarai ne da  suka   faru   a  tarihin zamanin  jahiliyyar  larabawa wasu  kuma   zamanin  bayyana  da kuma bunkasar  musulunci.

An karkare  da cewa wanda ya fara ko suka fara   rubuta  littafin  sun fara   bisa  wani   bacin rai ne. saboda salon yadda  suka faro   rubutun  dashi

Asalin labarin ya fara ne  daga wani  sarki mai  suna shahr yar wanda ke  mulkin wata  Babba kasa  wata rana  dan uwansa wanda  shima sarki ne. a  wata kasar    sarkin mai  suna  shahzaman.ya  aiko masa yaje yana son ganinsa.ya yi  ban kwana da  fadarsa da matansa da barori ya kama  hanya.har ya  yi nisa  sai ya tuna da yayi mantuwa,ya  dawo   a sukwane  don ya  dau abin day a manta  a fadarsa.yana  isa sai  ya ike matarsa  da wani bawansa. A bisa  gadonsa, nan ya kasha  su.

Ya  isa wajen  wancan sarki cikin Bakin cikin abin  da ya  gani.ya   shiga   wata irin damuwa. Wadda ko  ina  bai iya fita  a fadar inda yazo  bakunta. Wata  rana  yana  zaune a  dakin bakin da  aka  aje shi  shi  shi kuma mai masaukin bakinsshi  ya tafi kilisa.  Sai ga  matarsa  da wani  mutum bawan sarkin  sun  fito  suna  watayawarsu.

Wannan yasa  zucizyzrsa   tace  ashe wannan cin amana  ba wai a gidansa kawai  ta kare ba.don haka   sarki   shahzaman  na dawowa sai ya bashi  labarin abinda ya gani a gidansa  da kuma  wanda shima ya gano  gidansa  day a baro.

Sarki   shahzman na  dawowa  daga     kilisa. Abokinsa sarki  shahryan ya  kwashe  labarin abin day a gani ya faru gidansa ya  fada masa. Ya  kuma  bashi  labarin abin da   ya  same shi  a gidansa.da  bakin cikin dake  damunsa tun day a zo.suka   tsara  yadda  sarkin zai boye  a dakinshi  ya yi   kamar ya tafi  kilisa domin ya gane   ma idonsa  dil.

Haka  suka yi   suna  boye  a inda  suke  sai ga matar  sarkin nan da wani bawan gidan sun  fito  sune  sheke  ayarsu, wannan  abu ya sasu   cikin wani bakin ciki. Suka  shirya  fita  garin su  shiga uwa  duniya  har sai sunga wani  abin takaicin  day a  fi nasu.

Bayan sun  bar fada  suka dosa   tafiya  a dokar  daji.sai   suka   zo wani waje da dare  yayi masu.  Suka daure  dawakansu. Suka hau saman kololuwar  itace   don su huta kafin safe  suci gaba  da tafiya.can  tsakar  dare sai ga wani  aljani ya dawo  daga tafiya  shima ya sauka kasan itace  domin ya  huta.bayan ya  zauna  sai ya dauko  wani  akwati ya fito  da wata  yarinya  kyakykawa. Yace mata  kema  fito  ki  motsa  jininki  kafin  in  danyi   barci.

Yarinyar  ta  fito   ta gyara  gashin tat a kuma  dauko jita  tana kadawa  har Aljanin na yayi barci. San nan   ta farad an yawo tana motsa kafarta.daga  kanta  da za tayi sama. Sai ta  Hangi  wadan nan sarakuna biyu. Nan take tace ku  sauko. Suka  fara   gardama  tace koo  ku sauko ko in tayar da wannan aljani daga barci  ya halaka ku.

Daga  nan  sai suka  sauko  . suna  saukowa tace  kowa  cikinsu   sai  yayi amfani  da ita.ko kuma  ta tayada aljanin nan ya kasha su.nan  su  kayi bayan  sun yi  tace kowa ya  bata  zobensa  suka bata. Ta dauko wata jaka ta hada  da wasu zoben  dake  aciki.tace  kune  na saba in da kuka yi amfani  da ni ina ahannun wannan aljanin.

Ta  basu  labarin kanta da cewa   ita  diyar sarki  ce. A ranar daurin aurenta  wannan aljani ya sato ta.kuma yake yawo da ita  don kishi  don karma wani da namij ya aganta.tace amma tana wajenshi ta sadu  da  maza  sarakuna   saba in. har  dasu.tace  masu kusan in diya mace na son abu duk duniya  ba wanda ya isa ya hana ta  samunabin da  take so.

Wannan  labarin ya sa sarakunan  nan  suka dawo gida. Sun ji  wani abin da yfi nasu ban  al ajabi.sarki shahzaman ya zuwa ya  aka kasha matarsa  da bawan da suke holewa tare.ya kuma ce   bai karaaure. Amma  duk Dare  yana  son  a samo masa  budurwa wadda  zai kwana da ita da safe ya  kasha ta.

Haka ya rika yi tsawon zamani   har yan matan garin suka kare  wasu kuma suka gudu.suka koma wasu garuruwan.ya rage gidan  waziri kawai  yake  da wasu yan mata guda biyu Babbar sunanta  shaharzad  karamar sunanta  dunyazad.duk kaninsu  waziri yasa  masana sun karantarsu da ilmi so sai. Kuma  shaharzad ta rika  gwamuza  da baki in sunzo  gidansu tanajin labaran  fatake  da kasashe.

Wata  rana   waziri ya dawo gidansa ransa bace.ya yansa  suka tambaye shi lafiya? Ya fada  masu cewa  gobe  babu budurwar da zai kaima  sarki. Don duk garin bay an mata kodai ya kasha su ko kuma sun gudu.yaje kasuwar bayi babu, an bar kawo wa  tun da an san me ake  dasu a garin.kuma sarki sawa zai yi  a akshe ni in ban cika maganarsa ba zuwa gobe.

Sai babbar  diyarsa tace   Baba  gobe  ni za a kai.shahazad ta gamsar  da babanta gobe  a akaita. Nan  suka zauna  da jimamin daga gobe ba akara ganin  diyarsu.ta kuma kara dacewa gobe in zan tafi  zani tafi ne da kanwata  dunyazad.nan ma waziri ya shiga wani taskun nab akin ciki.Shahazad  ta  shirya  da kanwarta cewa   gobe  in munje .bayan mun gama abin da zamuyi  da sarkii ki roke ni  cewa  in dan  baku labari  kafin safiya  tayi.ni kuma  zan  fara

Wanshekare  sarki  da diyar waziri  suna  fada suna jiran  safiya tayi a tafi da ita  akashe.kamar yadda a ke yi.sai  Dunziyad tace yar uwata kafin safiya ta ida hauni yazo yagama aiki akanki ko zaki  bamu wani  dan labari daga labaran da kikia sani ?shaharzad  sai ta fara.kafin ta kai karshe  sai  rana tafito.

Sarki sai cewa  yayi bani kasha ki. Sai gobe kin gama wannan labarin.Daga  nan ne labarin  DARE DUBU DA DAYA YAFARA.Ta  rika  saka labari  cikin labari.wata irin hikima mai ban mamaki.ta  kuma rika   kawo  waka da kalaman  batsa. Don ta daga hankalin sarkin  ya  kara rike ta.

Da  wannnnan labarin na duk  dare ta sanya  sarkin yayi nadamar abin day a aikata abaya.kuma ya canza tunaninshi  na mummunar kallon da yekama mata. Kuma  ya shin fida adalci a kasar  sad a yankinsa baki  daya .ya kuma aure ta.labarin yak are  a dare dubu da daya  bayan a wata  ruwayar  sarkin ya mutu. A wata  kuma ya auri shaharyazad..Dare dubu da daya shine  littafin da  ba ai kamarsa ba  adabin duniya.kuma ba   ba a san waya rubuta  shi ba.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here