Martani: Gwamnatin Tarayya Ga PDP Ku Dawo Da Kudaden Da Ku Ka Sace

0

Daga Jamil Adamu Balarabe

Gwamnatin Tarayya ta bukaci jam’iyyar adawa ta PDP da ta cika ladanta na neman afuwar ‘yan Nijeriya ta hanyar dawo da dukkan kudaden da aka sace daga baitil malin kasar a lokacin da take mulki kasar na tsawon shekara 16.

A cikin wata sanarwa da gwamnatin ta fitar a yau Talata a Abuja, Ministan Watsa Labarai da Al’adu Alhaji Lai Mohammed, ya kuma kalubalanci PDP da ta nuna lallai afuwar da take nema ta gaske ce ta hanyar sauya halayyarta na dawo da kudaden da aka sace lokacin mulkin jam’iyyar.

Gwamnatin ta fitar da sanarwar ne a matsayin mayar da martani kan wata sanarwa da tun da fari jam’iyyar PDP ta fitar, inda take neman afuwan ‘yan kasar game da kura-kuran da ta tafka a lokacin da ta mulki kasar na tsawon shekara 16.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here