Sa6on da PDP keyiwa Allah ne yasa Allah ya karbe mulki ya bawa APC – in ji Bafarawa

0

Daga Sulaiman Umar

Attahiru Bafarawa, tsohon gwamnan Sokoto, ya shawarci ‘yan jam’iyyar PDP su kara yawan addu’o’i da tuba ga Allah.

A cewar Bafarawa “Laifukan da ‘yan jam’iyyar PDP suka yiwa Allah ne yasa yanzu yake azabtar da su a hannun APC.

Bafarawa ya yi wannan furuci ne a yayin da yake jawabi a taron Jam’iyyar PDP shiyar arewa maso yamma ranar Asabar a Katsina.

“Allah baya kuskure, sabamar da mukayi ne yasa ya horamu ta hanyar karbar mulki daga hannun mu zuwa hannun APC” cewar Aliyu Sadiq Bafarawa

See also  DANLAMI KURFI YA FICE DA GA APC YA KOMA PDP

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here