Sa6on da PDP keyiwa Allah ne yasa Allah ya karbe mulki ya bawa APC – in ji Bafarawa

0

Daga Sulaiman Umar

Attahiru Bafarawa, tsohon gwamnan Sokoto, ya shawarci ‘yan jam’iyyar PDP su kara yawan addu’o’i da tuba ga Allah.

A cewar Bafarawa “Laifukan da ‘yan jam’iyyar PDP suka yiwa Allah ne yasa yanzu yake azabtar da su a hannun APC.

Bafarawa ya yi wannan furuci ne a yayin da yake jawabi a taron Jam’iyyar PDP shiyar arewa maso yamma ranar Asabar a Katsina.

“Allah baya kuskure, sabamar da mukayi ne yasa ya horamu ta hanyar karbar mulki daga hannun mu zuwa hannun APC” cewar Aliyu Sadiq Bafarawa

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here