Yadda Aka Yi Wa Kalaman Shugaba Buhari Mummunar Fahimta Kan Matasa

0

Wasu ‘yan Nanjeriya na cigaba da fassara kalaman Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ta hanyoyi daban-daban, yayin da wasu mukarraban shugaban kasar suka ce an yi mummunar fahimta game da kalaman da shugaba Muhammadu Buhari ya yi cewa mafi yawan matasan kasar ci-ma zaune ne, sun fi son su ci daga sama.

Shugaba Buhari yana magana ne a taron kasashen renon Ingila dake gudana a birnin Landan.

Sai dai kalaman sa na ci gaba da tayar da kura a tsakanin matasan kasar musamman a kafafen sada zumunta na zamani.

Matasa da dama dai sun nuna damuwarsu kan kalaman da suka ce na zubar da kima ne, da shugaban ya yi.

Jim kadan, mai bai wa shugaban shawara kan kafafen watsa labarai Sha’aban Sharada, ya ce matasa da dama ba su fahimci kalaman Shugaba Buhari ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here