Harin Mubi: An Kashe Mutum 27 A Masallaci Da Kasuwa

0

Gwamnatin Najeriya ta umurci jami’an tsaron kasar da su tsaurara matakan tsaro a kasuwanni da sauran wuraren ibada a garin Mubi da ke jihar Adamawa.

Hakan ya biyo bayan matakin ne sakamakon wani harin kunar bakin wake da bam-bamai da aka kai wani masallaci da ke kasuwar garin Mubi wanda ya kashe akalla mutum 27 tare da jikkata wasu da dama.

Mataimakin shugaban kasar Farfesa Yemi Osinbajo wanda ya bada umurni ya kuma umurci hukumar agajin gaggawa ta kasa wato NEMA ta gaggauta samar da magunguna da sauran kayayyakin agaji ga wadanda lamarin ya rutsa da su.

See also  ONGOING CONSTRUCTION OF THE NORTHCENTRAL SKILLS ACQUISITION CENTRE IN KEFFI, NASSARAWA STATE!

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here