GWAMNAN JIHAR KATSINA YA BUƊE  MASALLACIN JUMA’A A MAKARANTAR HASSAN USMAN KATSINA

0

GWAMNAN JIHAR KATSINA YA BUƊE  MASALLACIN JUMA’A A MAKARANTAR HASSAN USMAN KATSINA

Daga Abdurrahaman Aliyu

Rt. Hon. Aminu Bello Masari, a yau 1 ga watan Yuni, 2018 ya buɗe  masallacin juma’a a makarantan kimiya da fasaha wadda akafi sani da Hassan Usman Katsina Polytechnic.

Gwamnan ya isa masallacin kafin fara sallar juma’a inda aka gudanar da sallar juma’a raka’a biyu tare da shi.
Wanda hakan ke gwada  cewa an buɗe masallacin.

Masallacin juma’ar, zai amfani dubban musulmi wanɗanda suka  haɗa da ma’aikatan da ɗaliban makarantar, kai har da sauran al’umma da suke kusanci da makarantar.

A lokacin buɗe masallacin, mai girma gwamna ya yi kira tare da fatan haɗin kan al’ummah musulmi baki ɗaya ba tare da banbancin aƙida ba domin kowane masallaci wuri ne na bautan Allah.

Daga ƙarshe ya kuma yi kira ga al’ummah musulmi baki ɗaya su kasance ‘yan uwan juna da ƙaunar juna, suyi kira tare da wa’azin da zai gina kyakkyawan fahimta tsakanin al’umma.

Daga Abdurrahaman Aliyu

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here