KUJERAR  MATAIMAKIN GWAMNA A MATSAYI DA TSARIN MULKIN  NAJERIYA

0

 

KUJERAR  MATAIMAKIN GWAMNA A MATSAYI DA TSARIN MULKIN  NAJERIYA

Daga  Danjuma Katsina.

Wani bincike da na gudanar  akan wannan matsayi na  kujerar mataimakin gwamna   shine matsayine  wanda  sai mai hakurin   gaske  da kai  zuciya  nesa  ke  iya  rike ta.  Sai  kuma wanda  ke  d a  wata  irin  fahimta da dangantaka  mai   karfin gaske  tsakanin  mai rike  da  ita  da kuma gwamnan  da suke mulki a tare.

Kujera da  matsayi ne  wanda  tsarin  mulkin kasa  ya  kasa bata  ko mai ita  wani   hobbassa  sai  dai  kawai  cewa .in gwamna  baya nan  ka  rike. Shima  wannan ba dole  bane in  gwamnan yaga  dama yana iya  baiwa  wani  ba kai ba. sai kuma duk  wani aiki da   gwamna ya  baka.

A  tsarin  mulki  a  matsayin  baka  da  hus na  wani  abu  da zaka iya  aikatawa. Sai  abin  da  gwamnanka  ya  baka.  baka  da ikon bada  umurnin  fitar  da kudi  ko  da kuwa  ficika  ce. In dai ba daga  cikin  aljifunsa  zai  fitar  ba.

Wannan  matsaya  ya  sanya  masu  rike  da  wannan  matsaya sai  ka samu  suna  fama  da  jama ar da suke  karkashinsu  a siyasance.  Suna  tsammanin  cewa  saboda matsayin  da suke  rike  dashi  na suna daga   gwamna sai  su. Don haka  suna tsammanin  duk  yadda gwamna  ya fantama  dole ne su fantama  a  hakan

A  wani  lokaci  idan mai   wannan matsayi   yace zai rika  kula jama ar  na siyasa   sai  kaga yan  tsurku   sun fara  kai  suka  ga gwamna  cewa  lallai  mataimakin  nasa  yana masa  wata makarkashiya ko  yana  shirya  msa  zagon kasa  baka Ankara  sai  kaga an  fara  yakin  sunkuru  da gaba   in ba akai  zuciya nesa ba  . sai  kaga  mataimakin gwamnan  ya zama abin tausayi.

Irin  wannan  sarkakkkiya  wanda    mataimakin  gwamna kan shiga  shi  yasa   a baya  akayi  ta  samun masu rike da matsayin  a  baya  sun  rika kira a  soke  kujerar,  wanda  ya fara wannan kiran a  baya  shine Alhaji  tukur  jikamshi  lokacin  yana mataimakin  gwamna .zamanin marigayi  umaru musa yar adua.  Da  aka  shiga  tsakaninsu  sai  da  Alhaji  tukur jikamshi ya  zama abin  tausayi

Irin  wannan  sarkakkiya  da  matsala  ya  sanya ake  samun rigingimu  tsakanin  gwamnoni  da  mataimaknsu  a jihohi  daban daban ,kamar  misali  kwanan nan a kano  tsakanin   ganduje  da farfesa  hafiz  wanda  aka  ruwaito  mataimakin na wasu  zantuttuka ga  mutanensa. Har  yana cewa  ba a  sake tsayawa  takara  tare  dashi ba. da abin day a faru  kwanan nan a Bauchi  inda mataimakin  ya ajiye  yace  gode  da damar  da aka  bashi,da  yadda  ya  taba  faruwa lokacin  bafarawa  na gwamna   wammako na mataimaki a jahar sokoto..

A  karkashin  kasa   jihohi  da  yawa  na  fadan sari  ka noke tsakanin  gwamnansu da  mataimakansu   kuma  da  yawa  suna cin  dudduniyar  juna,wannan  ya  sanya  gwamnoni  da yawa basu  son suga cewa  mataimakansu  sun  gaje su.  Wasu  na cewa  misalai    da aka samu na mataimaka  na gadar gwamnoni . in sun  hau  sukan kokarin  rama cutarwar  da  aka yi  masu   lokacin  suna  biyayya. A  sokoto  da wammako  ya zama gwamna   said a  ya  hana bafarawa  sakat a  siyasance haka  da  mamuda  ya zama gwamna  said a  ya hana yarima sakat  a  jahar  zamfara.  Ga  abin dake  faruwa   yanzu  a  jahar kano  tsakanin  kwankwaso  da  Ganduje,

Kujerar    mataimakin  gwamna  wani  matsayi  ne na iya ruwa fitar  da  kai.in kuma  bakayi  taka  tsantsan  ba.  to  zaka  shiga rububi  don  gwamnanka  zai  kuble  ka  kuma  baa bin  da  zaka iya a  tsarin mulki

Sai  dai  a  ganka  da yawan   jami   an  tsaro  da  jiniya  in kana so .wadanda suma  tsarin mulki  ne ya baka su.  Amma  a ciki ba komai  sai  fankam  fayam.domin  hakkinka   na ofishin iya wanda  doka  ta  baka ,in baka  basu  iya rike  maka  danginka balle  siyasarka .kamar  yadda  binciken  da  nayi  ya tabbatar mani.

Wani  mataimakin gwamna day a samu matsala da gwamnansa  ya  shaida  mani  cewa.da  gwamnansa  ya rike masa komai   saboda  munafukai  sun shiga  tsakaninsu.yace  sai  da  cefane  irin wanda ya kamata ayi a gida na ya  nemi ya gagare ni.’’inji  shi

Kamar  yadda  nace , matsayin  iya  ruwa  ne  fitar  da  kai, idan ka amsa   dole  kasan  matsayin  da  tsarin mulki  wanda ba komai  bane  da  ya  wuce bin  abin da gwamnanka  keso.  Daga nan  ya  zaka  zauna da  mukarraban gwamna lafiya  kamar yadda  wani   tsohon mataimakin  gwamna ya shaida mani .’’ zaka yi   ta  gani  da ji  daga  wajensu[jami an gwamna]kuma  ba ruwansu da kai  don haka sai ka kai  zuciya  nesa’’

sai  kuma  ya  zaka  tafiyar  da  siyasarka ?  wanda  yafi  wahalar sha ani da  kuma  tsaka mai  wuya.in ka rika  biya su  da  tara su. Da  taimaka masu .a  ce  ma  gwamna kana  da  manufar  da  ta sanya kake  hakan  in akai  nasarar  hada ku   fada.na lahira  sai fika jin dadi,in kuma  ka kyale mutanenka  ace  ka watsar   dasu anan  wani  yanayi ne na  gaba kura  baya  siyaki.

Rashin   wani  takaimemen  matsayin  da  tsarin  mulki  ya baiwa  kujerar   ya  sanya  idan kuna  dasawa da  gwamnanka  sai  baka  wata ministiri  yaceka rika kula da  ita, sannan  ya rika baka wasu hukumomi  yace   kai ne  shugabansu , ya  kuma rika sanya  ka kana  jagorantar  wasu kwamitoci. Duk  wannan  in wata matsala ta tashi  gwamnan na iya  kwace su  cikin kyaftawa  da    basmallah. Kuma  ba  yadda  zaka  iya.  Baka kuma da  ta  cewa

Wani  tsohon mataimakin gwamna da nayi  Magana dashi, ma anar kujerar  sai  yace  ‘’ kujera  ce  ta biyayya ,wakilci, dan aike da kuma  jiran  me za a saka ,da aikata abinda  aka ce ma kayi ,ya kara  da  cewa  kujera ce  ta  hakuri da  amfani da  hikima ka zauna da  kowa lafiya’’

Bincike na  ya  tabbatar  mani  wasu  mataimakan gwamna  za suyi  ta hakuri,amma da  an  bar  gwamnatin  babu  ruwansu  da gwamnansu .don suna  tuna  cutarwa da  gwamnan yayi  masu. Nayi Magana da  mataimakan  gwamna biyu,wanda suke cikin wannaan koken .  daya  ya  shaida mani cewa ‘ Duk  halin  da na shiga   gwamna na ne ya saka ni    sai  fara kawo  hujjojinsa.’’  Dayan kuma  ya  shaida mani  cewa. ‘’  yanzu  zaman kai na nake  nayi  biyayya a lokacin da  muna gwamnati  kamar yadda tsarin mulki  ya  bani  to  yanzu  ba gwamnatin ! sai  kuma  in ci gaba da biyayya?ga wa”

In kaga dan siyasa a kujerar  mataimakin gwamna   abu  uku yake nema wajen ka. Shawara, tausayawa, sai  addu a.

Danjuma Katsina . mawallafi/ dan jarida ana samunsa a 08035904408 email .katsinaoffice@yahoo.com.twitter @danjuma katsina

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here