DAN NAJERIYA YANA GABATAR DA DARASI A CIKIN MASALLACIN ANNABI
A GARIN MADINA:
Daga. Muhammad Bello
Idan ba’a manta ba shekarun baya Dr.Ibrahim R/lemo ya taba gabatar da irin wannan darasi a lokacin yana karatunsa na PhD a jami’ar musulunci ta madina,amma a wannan shekara sheikh Magaji falalu Zarewa shine wadda Allah ya gaddara zai fadakar a wannan shekara
A Bana ma Hukumar Kasar Saudia ta bada daman Karantar da Alhazai da Harshen Hausa a cikin Masallacin Manzo dake madina.
Kullun: tsakanin Magriba da Isha’i.
Wuri: Kofar Sarki Abdulaziz cikin Haramin Madina.