DAN TAKARAR GWAMNA ZAI CIWO BASHI MAI TSADA

0

DAN TAKARAR GWAMNA ZAI CIWO BASHI MAI TSADA

 

Daga Taskar labarai

 

Wani Dan takarar gwamna a Katsina a wata jam’iyya na tattaunawar yarjejeniya da wani attajiri daga wajen jihar Katsina don ya zuba jari na ba da kudin da za a ci zabe shi kuma a bashi ragama mai karfin gaske a tafiyar da mulkin da kuma biyanshi kudin shi da riba mai yawan gaske.

 

Wata majiya ta shaida mana cewa, an kiyasta lissafin abinda ake tsammanin za a kashe da abin da ake bukata a wajen sa.

 

Majiyarmu tace wannan dan jari hujjan ya amince zai zuba jarinsa a zaben na Katsina don ya samu karfin iko da ribar da yake jin zai samu.

 

Majiyarmu tace an daddale akan ribar da za a bashi an kuma daddale akan mukamai na gwamnati da za a bashi, don su sa Ido ga ayyukan da za a Rika bashi.

 

Wani abin takaici wanda ake tattaunawar da shi ya zuba jarinsa a zaben sam-sam baya da alaka da Katsina da mutanenta ta kowace hanya.

See also  ASALIN SARAUTAR SARKIN KUDIN SARKIN KATSINA.

 

A lissafin su, Buhari zai fadi zabe, Don Haka Katsina za ta zama ta mai rabo, za a zo da abin arziki a watsa kamar yadda ake watsawa yan tsaki tsaba, daga nan Al’ummar Katsina sai su shiga wasoso, daga nan sai a lakumen zaben.

 

Majiyarmu tace an yi zama biyar akan lamarin a garuruwa daban-daban an kuma cimma manufa da matsaya. Ciniki ya Shiga sai bayar da awalaja, an yi cinikin makomar Katsina.

 

Za a shigo masu da kudin bashi a watsa, don suyi wasoso kamar Yan tsaki.

 

Taskar labarai zamu Kara zurfafa bincike, kuma mu fallasa komai daki daki dalla dalla.

_________________&_____________________________________

Kana son labarai na musamman? Bincike na musamman? Jeka turakar Taskar labarai dake www.taskarlabarai.com da sauran turakar sada zumunta na Taskar labarai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here