KO  INJINIYA  KABIR BARKIYA   ZAI  CHANZA HALI  IN YA  ZAMA SANATA?

0

KO  INJINIYA  KABIR BARKIYA   ZAI  CHANZA HALI  IN YA  ZAMA SANATA?

Daga  Taskar labarai

wani  bincike da  jaridar  Taskar  labarai  ta yi  a kan rayuwa  da aiki  da  injiniya  Kabir  Barkiya,  wanda yake neman  kujerar  sanata  a Katsina ta  tsakiya karkashin  jam’iyyar   APC  ya  nuna shi  ba mutum  ba ne  wanda  ya dace  da rayuwa  ta  siyasa.

Barkiya   wanda  yayi  aiki  har  ya kai babban matsayi  a gwamnatin  tarayya  har ya  rike hukumar  FERMA,  daya  daga  cikin  hukumomin masu  tasiri  a gwamnatin  tarayya  kuma a lokacin  ya  taka    rawar  azo  a gani  a  mukaman  da  ya rike.

Bayanan sa  na  in da  yayi  aiki   suna  da kyau  sosai , domin  an shaide  shi  da aiki  tukuru  da  yin mai inganci  da tsare  ka’ida da  kamanta  gaskiya .

Yayi   aiki  cikin  mutumci  ya kammala a mutunce. Ana kuma tuna shi ayyukan alheri  da ya bari a inda  yayi  ayyukansa.

Amma rayuwarsa  da  sauran inda  ya fito  fa?  tawaga  mai  karfi  daga Taskar  labarai  ta yi  tattaki  har  zuwa  karamar  hukumarsu  ta  kurfi  da  a  garinsu na  haihuwa  Barkiya, abin  da  ta gano  shi ne  sam baya  tare  da  mutanen karamar  hukumarsa.

A  garin  Barkiya sun ce  baya  zuwa  garin daga  lokacin zabe  sai  wani  lokacin na zabe ba su  san shi ba, sai  dai  fosta  in ance  zai yi  takara.

Fastarsa  ta  farko  da  ya  nemi  jam’iyyar  PDP  ta  tsaida shi  takarar  gwamna  da kuma   yanzu  da aka ce  zai  tsaya  takarar  Sanata a APC.

Mun zanta  da shugabanin  matasan Barkiya zantawa da  aka yi  cikin raha har da daukar  hotuna na bidiyo da kuma hoto  maras motsi. Sun fadawa  ‘yan jaridar  mu cewa duk cikar  Barkiya  da batsewarta, bai  taba samar wa wani aiki ba koda  kuwa  na shara ne.

suka ce duk aikin da  yayi a Abuja da  mukaman da ya rike da damar da ya samu ba  wani  dan Barkiya  da ya amfana da wannan damar, matasanmu  sun gama karatu  suna  son su wuce ba taimako, wasu sun gama suna son aiki ba aikin,
hatta  irin kuratan  soja, dan sanda ko sauran masu kaki, babu a duk  fadin Barkiya. Don kauye ce  sai da  wanda  zai tsaya  masu. Wanda  Allah  yayi wa  daukakan ya tsaya bai  damu ba.

Munje   asibitin  garin, wanda muka  gani tana cikin hali tana bukatar  taimako, shima ba wanda  zai  taimaka, wata  kungiyar  kasa da kasa na aiki amma aikin nata  ragagge  ne, ma’aikatan  wadanda wasunsu  yan asalin yankin ne, suna aiki da kishi  da   yin dubarunsu  na  yadda  za su iya  gudanar  da  asibitin  da  kan kansu, don in sun bari  ta rushe  sune  suka  rasa.

Ko Barkiya  ya  taba taimaka masu?  Sam-sam koda  kuwa da  kwaran kafinol  ne guda  daya.
mun  samu  labarin wutar  garin  ta  taba lalacewa, sai dai  akwatin taimako  suka  daga.

“Nawa  Injiniya Kabir Barkiya  ya  bayar?”   ko kwabo  inji  wadanda  suka nemi  tallafin har aka gyara.

Mun je  wani  gidan kasa kusa  da  gidan maigari, an tabbatar  mana shi ne kadai  gidan da Injiniya Kabir Barkiya  yake  da shi duk barkiya, gida ne na kasa da mahaifinsa ya gina masa  lokacin da za ai masa aure, nan yayi  zaman  angwanci  da amarci  da amaryarsa ta Ladar  noma.  Gidan  yana  nan yadda  yake  sama da shekaru talatin da  suka wuce.

Wani  dan Barkiya  yace  “kana ganin zaku  iya tsammanin wani abun kirki  daga wanda  ya yi  watsi  da mahaifarsa? ya manta  da  mutanensa?  ya  juyama asalinsa  baya?”

Kaje  ka yi  nazari  inji  wani  dattijo a garin  Barkiya, wasu  a garin sun shaidawa  tawagar  jaridar  cewa, sun ji wai  yana da  kirki  amma  inuwar  giginyace   na nesa ka shata, sai  kuma  ‘yan uwansa  na kusa.

Mutanen  garin Barkiya  al’umma ce  mai  kokari, manoma  kuma  ‘yan kasuwa, an tabbatar  mani  suna  da  hazaka a wajen neman karatu. kuma  suna  zarra  a duk  abin da  suka  sanya a gaba, musamman in  sun samu mai  tallafa masu, fitattun mutane  sun fito  daga mazabar daga  cikinsu har  da dan majalisa mai wakiltar   Dutsinma  da Kurfi, Alhaji  Danlami Kurfi da   shaharraren  dan jaridar nan  edita  a  kamfanin Primium Times mai  suna   Ashafa  Murnai  Barkiya.

Barkiya gari ne  mai  muhimmaci, wanda  ‘yan siyasa  da ‘yan garin suka  banzatar  da  muhimmancinsa a nan ne aka  haifi  Injiniya  Kabir  Barkiya  dan  takarar  Sanata  a Katsina ta tsakiya a karkashin jam iyyar APC.

Ko zai canza halinsa in ya samu  nasara?

__________________________________________________________
Taskar labarai jarida ce dake da cikakkiyar rijista dake bisa anar gizo www.taskarlabarai.com da kuma kafofin sada zumunta na Facebook da Twitter da Instigram da Youtube da Whatsapp a lamba 07043777779

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here