GWAMNA GANDUJE YA JAGORANCI KONA JABUN MAGUNGUNA DA KUDINSU YA KAI MILIYAN 360
Daga Ibrahim Hamisu, Kano
Gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya jagoranci bikin kona jabun magunguna da kwayoyin shaye shaye wanda kudin su ya haura N360Million.
Jami’an tsaro da suka hada da HISBAH, KAROTA da NDLE da hukumar ‘yan sanda su suka kama, kuma aka kona su a harabar hukumar NDLEA,
Gwamna Ganduje ya jaddada kudurin gwamnatin sa na ganin an shawo kan matsalar shaye shaye a Kano,
A nasa jawabin Dr. Ibrahim Abdullahi shugaban hukumar NDLEA reshen Kano ya yabawa Gwamna Ganduje bisa yadda yake yaki da miyagun kwawoyi a jihar,
A yanzu da Kano take a matsayin ma 6 a jihohin da ake shaye shaye wanda kafin Gwamna Ganduje, jihar Kano ce ta daya shekaru biyar da suka wuce.