TSADAR RAYUWA: AN FARA SATAR GARIN TUWO A KANO

0

Mazauna Unguwannin Kurna, Dandishe da Gobirawa dake Karamar hukumar Dala ta jihar Kano sun koka bisa yawaitar satar garin tuwo a wajen masu nika a jihar.

Jaridar PRIME TIME NEWS ta rawaito cewa mazauna unguwannin sun yi korafin yawan bacewar gari a wajen nika a yan kwanakin nan, wanda hakan ya haifar da damuwa tsakanin mutane, musamman ganin yadda tattalin arzikin kasarnan ke cikin mawuyacin hali.

Haka kuma rahotannin sun bayyana cewa yawancin wadanda lamarin ya shafa, masu karamin karfi ne wadanda baza su iya siyan shinkafa ba sai dai su ci abin da ya shafi gari musamman masara da gero, wanda dole ne a nika shi kafin a sarrafa shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here