Gwamna Ganduje ya bada umarnin rufe makarantun Kano
Daga Ibrahim Hamisu, Kano
Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje ya bada umarnin rufe makarantun jihar baki daya.
Kwamishinan ilimi na jihar Muhammad Sanusi Sa’idu Kiru ne ya sanar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a daren jiya Talata.
Ƙiru ya yi kira ga iyayen yaran da ke makarantun kwana da suyi hanzarin dawo da yayansu gida a yau Laraba.