Aika-aika ne tsantsa yunkurin Gwamnatin Kano na rushe gadar kofar Nasarawa

0

Aika-aika ne tsantsa yunkurin Gwamnatin Kano na rushe gadar kofar Nasarawa- ja’afar Sani Bello

Daga Ibrahim Hamisu, Kano

Ɗan siyasar nan da ya nemi jam’iyyar PDP ta tsayar da shi takarar gwamnan jihar Kano a zaɓen shekara 2015 Jafar Sani Bello ya bayyana ƙudurin gwamnatin jihar Kano na rushe gadar sama ta ƙofar Nasarawa a matsayin aika – aika kuma awon igiya.

Jafar Sani Bello wanda ya yi shuhura wajen bayyana raayinsa a fili ba tare da tsoro ba, musamman a gwamnatin Muhammad Buhari,

Ja’afar ya bayyana hakan ne a shafinsa na facebook a matsayin martani ga shirin gwamnatin jihar Kano na rushe gadar saman.

Ya kara da cewa “Rushe gadar Kofar Nassarawa Yanzu aika-aika ne, awon Igiya” In ji Jafar Sani Bello

Wannan dai yana zuwa ne a dai-dai lokacin da al’ummar jihar Kano ke bayyana ra’ayoyinsu akan bayanan da kwamishinan yada labarai cewa zaa rushe gasar a sake wata sabuwa saboda rashin inganci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here