๐ฟ๐๐ข๐๐๐ง๐๐ง ๐๐๐ก๐๐ฎ๐๐ฃ 450: ๐๐จ๐๐ ๐๐ฃ๐๐ฃ๐, ๐๐๐ก ๐๐๐ฎ๐ฃ๐ ๐ฟ๐ ๐๐ข๐ข๐ ๐๐๐ ๐๐๐!
Daga Suleiman bala idris
Wannan labarin da zaku karanta ya faru da gaske, ba tatsuniya ko ฦage ba ne.
Ni ne mutum na farko da ya fara shiga tsakanin Zainab Ibrahim da ‘yan jarida (bayan ta fara shiga rigingimu). Zainab Ibrahim wacce ta shahara da suna Ummi Zee Zee, da kanta ta buฦaci hakan daga gareni, duk da kuwa a lokacin bai fi shekara biyu da na shiga harkar Jarida ba.
Wani abu ne ya faru a watan Janairun shekarar 2009 lokacin ina Editan Mujallar MATASA (wata Mujalla da ta yi tashe lokacin mulkin Marigayi ‘Yarโadua) wacce kamfanin Katsina Media Links mallakin Mallam Danjuma Katsina ke wallafawa.
Mun buga wani labari a shafin ๐๐ข๐ถ๐ณ๐ข๐ณ๐ถ๐ธ๐ข ๐๐ข๐ช ๐๐ถ๐ต๐ด๐ช๐บ๐ข, mai taken: ๐๐ฅ๐ฅ๐จ๐ฅ๐ข๐ง ๐๐ก๐๐ฒ๐-๐ฌ๐ก๐๐ฒ๐ ๐๐ ๐๐๐ญ๐๐ฌ๐: ๐๐๐ซ๐ฎ๐ฌ๐ฌ๐ ๐๐๐ ๐ ๐๐๐ฒ๐ฎ๐ฐ๐๐ซ ๐๐ข๐ฅ ๐๐๐ฒ๐ง๐.
Ni na rubuta labarin bayan dogon nazari kan yadda harkar shan miyagun ฦwayoyi ta raunata rayuwar mawaฦi Lil Wayne, kuma a wancan lokacin shi ne abin koyi ga matasa.
A kan wannan labarin ne Ummi ta kira ni, tana nuna rashin jin daษi, a cewarta wai mun zagi mawaฦi mai tasiri a duniya. Ni ban ma santa ba, saboda ban san kowa a harkar fim ba. Ta gama faษin ra’ayinta sannan ta kashe waya. Kafin ta fara magana ta gabatar min da kanta da sunan Zainab Ibrahim (ba ta ce Ummi Zee Zee ba).
Bayan kaman kwana biyu, sai aka sake kirana da wannan lambar ta Glo, ban yi ‘saving’ layin ba, amma ina gani na iya tuna an kirani da lambar. Tana magana cikin isa da izza ta ce, Zainab ce. Na ce, Allah sarki! Nan ne ta fahimci ban ma yi ‘saving’ lambar ba. Ta cika da mamaki, ta ce, ‘ka yi laifi biyu. Na farko kun zagi Lil Wayne, na biyu ka ฦi saving lamba ta.’ Sai muka yi dariya.
Lokacin da za ta kashe waya, bayan mun gama magana, sai take ce min ai ‘yan jarida na da ฦarfin ikon gyara abu ko ษata shi. Za ta so idan ta dawo Nijeriya mu tattauna. Lokacin tana ฦasar Misra ta je hutawa. Ni a lokacin ba ta ita ma nake ba, saboda kaina ya ษau zafi, muna kici-kicin tsara Mujallarmu ta watan Fabrairun 2009.
Bayan watanni kaman uku sannan na gane ashe Ummi Zee Zee ce Zainab Ibrahim ษin da ke kira. A ranar da wani ke faษa min cewa ita ce, a rannan ta sake kirana a waya. A ranar muka fara haษuwa. Ta gabatar min da wasu ฦorafe-ฦorafe kan abubuwan da ake wallafawa a kanta. Ta nuna min wasu gidajenta a garin da muka haษu (ba Kano ba).
A lokacin da gaske akwai ‘yan kuษaษe hannun Ummi, sai dai ba zan iya cewa sun kai nawa ba. A lokacin tana hawa motoci guda shida da ”customized number’ mai ษauke lambobi Zee Zee 1, 2, 3, 4,5, 6. Da su take yawo a Kano, Kaduna da Abuja.
Mu’amalata da Ummi kawai harkar jarida ne. Duk da a lokacin ba ni da wata cikakkiyar gogewa a harkar Jarida, amma na yi ฦoฦari wurin ba ta shawarwarin da nake ganin ba kawai a harkar Mu’amala da ‘yan jarida ba, zai taimaka mata wurin muโamala da mutane da sauฦake rigimar da take faษa wa.
Lokacin da tsohon saurayinta ‘ฦan Chana’ ya sakota gaba, ni ke bada shawarar me za a yi, me kuma za a rubuta. A lokacin tana tsananin bani tausayi ne, saboda irin tarin rigingimun da ke kanta. Har ta kai wasu cikin ‘yan uwanta sun sanni.
Ta sake fuskantar sabon babin rigima ne bayan da ta koma Fatakwal (Porthacourt) da irin abubuwan da suka shiga tsakaninta da su Timaya, Jonah de Monarch da Weatherman. Da gaske ne Timaya ya amshi kuษaษe hannunta da sunan waฦa da soyayya.
Akwai wani abu da ya faru har ta kai na shiga tsakani. Jonah De Monarch wanda suka yi waฦar ‘Janglover’ tare ne ya so ya damfareta, ฦarshe dai ni aka nema na shiga tsakani, har sai da ta kai Jonah ya yi ta surfa min zagi. ฦarshe na ce mishi, ni ba ษan fim ba ne ko mawaฦi, ni ษan Jarida ne.
Na kawo kaษan cikin waษannan misalin ne don na tabbatar da cewa da gaske ana iya damfarar Ummi, saboda tana da saurin yarda. Amma ko ni ban yarda cewa an damfareta Miliyan 450 ba.
Akwai wasu ‘yan jarida da ta amince musu ta ba su kuษi (ta faษa min nawa ta basu) amma suka wallafa wasu hotunanta marasa kyawun gani da Timaya da Jonah de Monarch.
Saboda gajiya da shiga rigima ne dole ฦarshe na daina shiga waษannan rigingimun muka kuma daina magana da Ummi. Kuma ma dai, lokaci ya fara yi min ฦaranci; ga aiki, ga karatu duk a lokaci guda.
Kafin mu daina duk wata mu’amala da ta shafi harkar jarida da Ummi na ba ta wasu shawarwari kan yadda za ta kaucewa ci gaba da faษa wa irin waษannan rigingimun. Musamman ma lokacin da labarin ‘soyayya da IBB’ ta yi ta yawo.
Mutane da dama sun tambaye ni kan me ke faruwa har Ummi ke son kashe kanta. Na yi ฦoฦarin bada amsa da ‘ni ma ban sani ba, rabona da yin waya da Ummi tun 2012’. Don haka nema na yi ฦoฦarin nemanta don jin dalilin da ya sa take son kashe kanta, wannan kafin labarin damfara ta fito kenan.
Zai yiwu ba gaskiya bane an damfareta Naira Miliyan 450, amma a yanzu ita ‘patient’ ce ta ‘depression’. Mai jinya ce da take buฦatar taimakon duk wanda zai iya taimaka mata har ta dawo hayyacinta.
Kamar dai yadda ‘yan Nijeriya da yawa ke fama da jinyar damuwar da ba su iya sanar da kowa. Mutane sun faษi ra’ayoyinsu; masu kyau da munana. Gabaษaya mun manta cewa, idan ฦarya Ummi ta yi kan damfarar da ta yi iฦirari, kenan ana da cikakkiyar hujjar da ya kamata a taimaka mata ta ga likita ko ฦwararre kan harkar da ta shafi ฦwaฦwalwa.
‘Depression’ gaskiya ne, musamman ga mutumin da ya saba da kuษi kuma ya zo bai da su. Allah Ya sa mu gama da duniya lafiya!
Sulaiman Bala Idris
07-04-2021