SHARHIN: Katsina City News ZABEN SHUGABANNIN APC A KATSINA

0

SHARHIN: Katsina City News

ZABEN SHUGABANNIN APC A KATSINA

…A tabbatar Da An Yi Adalci

*Jinjina Ga Gwamnan Katsina Da Alhaji Muntari Lawal

@Katsina City News

Ranar Asabar 2 ga watan Oktoba, 2021 aka fitar a matsayin ranar da za a yi zaben shugabannin jam’iyyar APC na Jihohi.

Kwamitin riko na zaben shugabannin ya fitar da ka’idoji da kuma tsare-tsaren da ya gindaya, wadanda sune aka yi ta amfani da su a zaben shugabannin Unguwani da Kananan Hukumomi.

Har ila yau, Jihohi da yawa suna ta rikici kafin da bayan zabubbakan, wasu an shigar da kara daban-daban a kotuna, wasu na shelar za su fasa kwaryar garin don kowa ya rasa.

A Katsina cikin karfin ikon Allah komai yana tafiya lafiya lau da kudurin da Gwamna Aminu Bello Masari ya dauka, kuma yake aiwatarwa a aikace shi ne adalci.

Duk zababbunkan da aka yi, adalcin Gwamnan ya zama abin misali, wannan ya sanya jam’iyyar ta zauna lafiya a iya abin da jaridar nan ta sani.

Sallah daga Liman take gyaruwa, wannan ya sa Shugaban Kwamitin, Alhaji Muntari Lawal shi ma ya tsaya CAK a kan matsaya ta adalci, komai nasu suna yin sa ne a bude, kuma baje a bisa faifai.

‘Yan kwamitin baki dayansu da suke wakiltar ‘yan takarkari duk sun ce tafiyar su karkashin shugabancin Alhaji Muntari Lawal masha Allahu, ALHAMDULILLAH.

Yanzu kamar a ce a Sallah ce, an zo raka’ar karshe, kuma an yi Sujadar karshe, saura dagowa Sujada da Tahiya domin Sallama, Sallah ta kammalu ke nan.

See also  Yadda Aka Yi Wa Kalaman Shugaba Buhari Mummunar Fahimta Kan Matasa

Mu a jaridun Katsina City News muna kira a tabbatar da cewa, jam’iyyar APC a Katsina ta karkare da yadda ta faro a sauran zabubbakan.

Wato bin ka’idojin da aka faro da su, adalci da aiki da shi. Wannan shi ne zai gina jam’iyya mai karfi, wadda a dimokaradiyya jam’iyya ita ce ginshikin mulki.

‘Yan takara daban-daban sun fito, wasu kuma ana jiran fitowar su.

Kiran mu a kammala yadda aka faro, babu sa baki ba tursasawa ba katsaladan ba sanya ido.
A kyale kowa ya baje kwanjinsa, a kuma yi adalci.

A zabubbakan baya da Gwamna da mataimakinsa sun nuna kyakkyawan misali, abin alfahari, abin nuni, sun kuma kawo wa jam’iyyar APC kwarjini a Nijeriya.

Duk kasar nan an sanya wa Katsina ido a matsayin Jihar Shugaban Kasa, Cibiyar kulle-kullen siyasa, shin za ta kammala kamar yadda ta fara? Zabe cikin bin ka’ida, adalci da kwanciyar hankali?

A jaridun Katsina City News, wadda daya daga cikin muradin kafa ta, shi ne samar da ingantacciyar gwamnati a bisa tsarin dimokaradiyya.

Za mu sa ido daga yau 20/09/2021 zuwa 04/10/2021. Kullum za mu saki labari ko sharhi a kan zaben na shugabannin jam’iyyar APC a matakin Jiha.

Allah ya sanya a yi lafiya, a kuma yi adalci. Ameen.
Katsina city news
Www.katsinacitynews.com
Jaridar taskar labarai
Www.jaridartaskarlabarai.com
The links news
Www.thelinksnews.com
07043777779 081 37777245

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here