Mahaifiyar AA Zaura Ta Shaƙi iskar ‘Yanci A Hannun Masu Garkuwa Da Mutane

0

Hukumar DSS ta kwato mahaifiyar dan takarar jam’iyyar APC a Kano ta tsakiya, sa’o’i 24 bayan an sace ta a wani yanki mai nisa na jihar Jigawa.

A safiyar ranar Litinin ne wasu ‘yan bindiga suka kai hari kauyen Zaura da ke karamar hukumar Ungogo a jihar Kano inda suka yi garkuwa da mahaifiyar AA Zaura a gidanta da ke kauyen Zaura.

Engr. Abdullahi Garba Ramat shugaban karamar hukumar Ungogo ya tabbatar da faruwar lamarin amma ya ce jami’an tsaro ba su sanar da shi lamarin a hukumance ba.

Sai dai wani babban jami’in DSS da bai so a bayyana sunansa ba ya bayyana cewa dakarunsa sun kubutar da Laure da wata tsohuwa da aka yi garkuwa da su kusan kwanaki goma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here