DA DUMI-DUMI: ‘Yan ta’adda sun kai hari a shingen binciken sojoji dake kan iyakar Abuja da Nijar.

0

 

Wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton ‘yan ta’adda ne sun kai hari a wani shingen binciken sojoji da ke gindin shahararren dutsen Zuma Rock a jihar Neja a daren Alhamis.

 

Inda aka kai harin na da nisan kilomita biyu zuwa Zuba a babban birnin tarayya Abuja.

 

A cewar wata kungiyar tsaro ta Eons Intelligence a shafinta na Twitter, @eonsintelligenc, ta ce ‘yan bindiga da sojoji sun yi artabu da yan bindiga a shingen binciken ababan hawa da ke kan titin Abuja zuwa Kaduna.

 

Ta rubuta Kamar haha: “A yanzu haka ‘yan bindiga da sojoji sun yi artabu a shingen bincike da ke Zuma Rock Madalla, daura da babbar hanyar Kaduna zuwa Abuja. Yanzu haka dai jami’an tsaro na ci gaba da bin sawun ‘yan fashin…

See also  DAN TAKARAR GWAMNA A PDP NA NEMAN TALLAFI

 

A halin da ake ciki dai, wasu da suka shaida da lamarin sun bayyana yadda lamarin ya faru a shafukan su na sada zumunta. kamar dai yadda Jaridar Daily Trust Ta Wallafa A Shafin Ta

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here