APC KU FARKA KAFIN LOKACI YA KURE. Inji …Dan Majalisa Jabiru yau yau

0

@ katsina city news

Dan majalisar dokoki mai wakiltar Karamar hukumar Batsari, Alhaji Jabiru Yau Yau yayi Kira ga gwamnatin APC da kuma uwar jam iyyar ta kasa da dau matakin gyara da karatun tanatsu Kafin lokaci ya kure.

Dan majalisar yayi wannan bayanin ne, a taron Manema labarai da ya kai a ofishin yan jaridu masu aikawa da Rahotonni dake titin IBB katsina.

Dan majalisar yace, Rashin adalci shine tushen komi.yace irin halin da APC ke ciki shine ya taba samun jam iyyar PDP a zaben 2015.

Dan majalisar ya kara da cewa.yanzu a jahar katsina sanata ya fita da APC ya koma PDP , yan majalisun Tarayya bakwai sun fice daga APC haka ma wasu yan majalisun jaha.

See also  ƁARAYIN DAJI SUN SACE MANOMA MASU YAWA A YANKIN BATSARI

Yace wannan yanayin abin tsoro ne, kuma,ya Kamata,jam iyya da gwamnatin APC su shiga taitayinsu.

Jabiru yau yau yace,Rashin Adalcin da akayi masa wajen zaben fitar da Dan takara.jam iyya a jaha bata dau wani mataki ba,don haka suna a kotun tarayya.

Shafin Facebook na jaridun taskar labarai da katsina city news zasu saka cikakkiyar hirar a shafukan su.

Katsina city news

@ www.katsinacitynews.com

Jaridar taskar labarai

@www.jaridartaskarlabarai.com

The links news

@ www.thelinksnews.com

07043777779 08137777245

Email:katsinacitynews2@gmail.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here