Masu Yiwa Kasa Hidima Sun Kaddamar Da Allunan Gefen Titi Masu Kira Da Yaki da Cin Hanci A Yenogoa

0

Sashen Ci gaban al’umma na masu yiwa kasa hidima sun kaddamar da wani allon gefen titi wanda yake dauke da sakonnin yaki da cin hanci da yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa.

Masu Yiwa Kasa Hidima Sun Kaddamar Da Allunan Gefen Titi Masu Kira Da Yaki da Cin Hanci A Yenogoa
Masu Yiwa Kasa Hidima Sun Kaddamar Da Allunan Gefen Titi Masu Kira Da Yaki da Cin Hanci A Yenogoa

An kaddamar da allon ne a titin kasuwar Opolo dake, Yenogoa, jihar Bayelsa State.

 

Shugaban masu yiwa kasa hidimar Busayo Adepoju ya bayyana cewa sun yi haka ne don wayar da kan alúmma akan yaki da yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa .

 

Akwai sakonni daban da aka rubuta a jikin allon dake kiran al’umma akan kauracewa cin hanci da rashawa, da kwarmata masu yin haka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here