DANKARAMI YA KAWO HARI JIHAR KATSINA…..Ya kashe sojoji  

0

Muazu hassan

@ katsina city news

A jiya talata 6 /9/2022 mugun dan ta addar na dake da kyakykawar alaka da kariya ga gwamnatin zamfara ya kawo hari cikin jahar katsina.

Dan ta addar mai suna Dankarami Wanda yanzu yake watayawa shi da yaran shi a fadin jahar zamfara a tsanake.

Dankarami ya baro, sansaninshi dake zamfara da mayakanshi,ya kai hari a yankin Kankara.

Sojan sama, sun kai daukin gaggawa, Wanda ya jawo Dankarami, suka janye kuma suka rabu kashi kashi don komawa masaukinsu a zamfara

Wani gungun ne suna Kan hanyarsu ta komawa.suka kashe wasu sojoji biyu a yankin Danmusa.

Duk wani Hari mai muni a jahar katsina daga yankin zamfara ake shirya shi.

See also  Yan sanda sun cika hannun su da masu buga jabun kuɗi a jihar Katsina

Hatta harin da ya tarwatsa wata motar sulke a yankin shimfida ta karamar hukumar jibia.maharan suna gama ta asarsu, zamfara suka shiga.

Dankarami shine Wanda majiyarmu ta tabbatar da cewa yana kitsa kawo Hari babban birnin katsina don ya firgita garin.

Bamu da wani tabbacin, ko gwamnatin zamfara na tsawata ma wadannan sojan bante nata.

Wadanda ake zargin ana sulhuntawa dasu, domin tanadin zaben 2023.

Katsina city news

@ www.katsinacitynews.com

Jaridar taskar labarai

Www.jaridartaskarlabarai.com

The links news

Www.thelinksnews.com

07043777779 08137777245

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here