Wata Kotu A Legas Ta Aike Da Fasto Gidan Gyaran Hali Na Shekara Biyu

0

Mai shari’a Oluwatoyin Taiwo na kotun laifuffuka na musamman da ke zaune a Ikeja, Legas, ya yanke wa wani Fasto, Ayodeji Ibrahim Oluokun hukuncin daurin shekaru biyu a gidan yari.

An daure shi a ranar Talata, 21 ga Satumba, 2022.

 

Laifin Oluokun ya biyo bayan tuhumar da hukumar EFCC shiyyar Legas ta gabatar tare da kamfaninsa mai suna Peak Petroleum Industry Nigeria Limited a kan wasu tuhume-tuhume shida da suka hada da bayar da cak.

Majiya: EFCC

See also  Gwamnatin Tarayya ta yi alla-wadai da alkawarin da Atiku ya yi na buɗe bodoji idan ya ci zaɓe

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here