An tsinto gawa 9 a hatsarin kwale-kwale a Nijar – NSEMA

0

Akalla gawarwakin mutane tara ne aka tsinto daga wani hatsarin kwale-kwale da ya afku a karamar hukumar Shiroro ta jihar Neja a makon jiya.

Ku tuna cewa kimanin mutane goma yawancinsu ‘yan kasuwa ne aka tabbatar da mutuwarsu a wani hatsarin jirgin ruwa da ya afku a ranar Alhamis 16 ga watan Nuwamba.

Shugaban sashen bayar da agajin gaggawa na Hukumar Agajin Gaggawa ta Jihar Neja, NSEMA, Alhaji Salihu Garba ya shaida wa NAN a ranar Lahadin da ta gabata cewa ya zuwa yanzu an gano gawarwakin tara daga cikin goman.

See also  KOTU TA BAYAR DA BELIN SARKIN YAKIN NIGERIA DCP ABBA KYARI?

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here