Dakarun Taliban sun harbe ƴan bindiga masu garkuwa da mutane
Daga: Comrade Musa Garba Augie.
Hukumomi a Herat yammacin Afghanistan sun ce dakarun Taliban a wata musayar wuta sun harbe wasu ƴan bindiga guda uku da ake zargi masu garkuwa da mutane ne a yankin.
Kakakin Taliban ya ce mutanen da ake zargi suna satar mutane, sun ɓuya ne a wani bene wanda jami’an tsaro suka yi wa ƙawanya.
Mazauna yankin sun ce an shafe awanni ana musayar wuta ta hanyar amfani da ƙanana da manyan makamai.
Wasu rahotanni sun ce masu garkuwar, mambobin ƙungiyar IS ne.
Taliban ta yi alƙawalin tabbatar da tsaro a Afghanistan ta hanyar ɗaukar tsauraran matakai kan miyagun ayyuka da kuma fatattakar IS da ke kai wa mayaƙan Taliban hari da kuma ƴan shi’a.