Darussan Da Na Samu A Shugabanci A NUJ

0

 

Daga Danjuma Katsina

Nasara Da Kurakuran Da Na Aikata

An rantsar da mu da qarfe biyar na marece.an zabe ni  cikin   murna  da  farin  ciki,na  dau nauyin anje  gidan abincin  Al mara  I   dake  GRA.an ci  abinci kyauta. A daren na nemo  tsarin mulkin  kungiyar , wanda  akayi  sabo, don a tsarin kungiyar  ana  canza  mata   tsarin mulki lokaci  lokaci.ina  da  wajen  kala  uku,na samo  sabon  shafin  dana  fara  karantawa shine, aikin ofis  din mataimakin  shugaba na  jaha,

 

Sannan na duba wasu   dokoki  da ka idojin da  kungiyar  ta ginu  akansu,a shafin  day a shafi  abinda  aka  zabe ni  akansa.anan nagaan rubuta  cewa.aikina  guda  hudu ne  kawai,1.in taimaka ma shugaba  akan duk wani  aiki day a  sanya ni,2  inyi duk wani aiki da  kunguya  ta  sanya ni,3 In waklici  shugaba, 4 in rike   kungiyar  in bayanan.  A  wani  waje  aka kara  man  wan  aikin  akace idan  bisa  wani  dalili,  shugaban  ya  zakuda  to in zama  shugaba,

 

Da  na  karanta  wadannan   aiyuka da  aka ba wannan  ofis nawa.sai  nayi  alkarin  zan kiyaye su da  kare su  iya  iyawa ta.na kuma  sha alwashin b azan taba cin amanar  wanda ya  kawo  nib a.da kuma ayyukanda aka  dora  mani.abin  da na rike  har  zuwa  karshen  lokacin da  aka sake  zabe.kamar  yadda  zan  kawo shi a rubuce,

 

Na  kuma yi  tunanin  cewa yayan wannan kungiya  mutane ne  masu  bsira da ilmi. Wanda  zasu rika  yi mana  hukunci  ne  dai  dai  ayyukan da  muka yi  akan  tsari  kuma  bisa  adalci.don na  kara  shan alwashin  zan  yi  komai  a  tsakani na  da Allah,wa

 

A  na wa  tunanin a   lokacin, idan nayi  haka to   bayan  mun gama  lokacin da  tsarin  mulkin ya shata  mana,zan bar  shugabanci  kungiayar  ana  shaukin  in ciga  ba. Ko kuma  ina cewa  banyi  ana cewa sai  kayi.na  kuma  tsara  ma  kaina  cewa  zango  daya  kadai  zanyi.wannan  duk wani na tare dani  ya san wannan matsaya tawa..

 

A  daren da aka  rantsar  damu   na  tsara  kaf,yadda  zan tafiyar  da  rayuwa  ta a  shugabancin  kungiyar.a  taronmu na farko.wanda mukayi  a  gidan rdiyo,  shugaban da aka zaba  Abdullahi  izma ya  nuna,mana  yadda  zamu  sa  muhimmacin kungiyar  ta  cigaba  a  gabanmu.

 

Hakikia  ya zo da wani  irin kishi, wanda yak e son kishin ya shige mu  kuma ya  jagorance mu  akansa.ya zo da  kudurin muci  gaba,ya  kuma zo  da niyyar ya  za mu  tarihin da  babu  wanda  ya taba kafa  shi  tunda  kungiyar tazo  Katsina.

 

Muna   shigo muna  da rashin   yadda da junanmu,kowa na   zargin  dan  uwansa.don  haka ma kowane  taro  sai an dau  bayanin  taron,kafin a  dawo  sai  anzo dashi  an  buga  an  raba  ma kowa kuma  kowa ya tabbatar  haka akayi  a taron day a gabata.anba kowa  ya sanya hannu, ba a kuma aikata komai sai   abinda   dake  cikin  tsarin taron,

 

Wannan  kaida ce mai kyau, wadda   gaskiyar  Magana  rashin yadda ta sanya  muka dage ta rika tafiya  a ha ka,wanda  daga  baya da muka fahimci junanmu,muka  watsar  sai  da muka  shekara  sama da biyu bamu kara hakan ba, har aka sake  zabe.kuma  ba wanda ya damu ko  ya taba  daga kara,

 

Mun  zo  ba kudi, a lokacin kudin da  ake cirewa  na  ma aikatan  jarida  daga  albashinsu, aba  kungiya, ba a  cirewa.don haka  idan  aka  hada  sai  dai  duk aikin  da aka ba wani daga  cikin  jami an, kodai   wani  ya ranta ayi  ko kuma  shi wanda   aka  ba, ya ranta daga  aljifunsa,

 

Wannan  ya daga hankalin    IZMA,wanda ya same ni  har  ofis ya roke ni,in fito  da hanyoyin  samun  kudi,don  a fuskaci aikin kungiyar   nan  gadan gadan.Na  dau  masa  alkawarin  cewa  daga   lokacin  har  zuwa  lokacin  da  za a  samu  mafita.duk  abin  da aka nema a wajena  na kudi  zan  bayar.amma  kaidata  biyu ce a  rika  rubutawa.a  kuma rika  sanyo shi a   takardar  karshen   taron da mukeyi don  abin ya  zama  a bude  kowanne  cikin  zabbabbu   shugabannin ya  sani.wannan  daga  cikin  laifuka na. ina  bada  kudi ga kungiyar  don inyi  yadda  naso.

 

Wannan kuduri nawa  izma  ya kawo  shi a  taron  da muke  kuma  kowa yayi  murna da jin  hakan.mun tsara  ziyarar  manya,jihar  da neman  goyon bayan su.wanda  duk  mukayi  a cikin nasara.ziyarar  kuma  ta shelanta cewa   NUJ  tayi  sabbin  shugabanni   da  suke  niyyar kawo canji.

 

Duk  taron  da muke  a gidan rediyo muke yinsa.wata  ran   IZMA  ya  sameni  da  safe  a ofis nawa yace   ya  za ai mu  sami  wanda  zai dau  nauyin kama mana  ofis  wanda  daga nan  zamu rika tafiyar  da al amurranmu.ya yabi  hakurin yan  gidan rediyo  damuke  taro  a wajensu.yace  muna masu tashi na kamaka kuma mu takura su. Amma su  hakura.yace  kamata yi  yai muna da ofis,

 

Na  fada  masa cewa  muje   Alhaji  bilya  rimi  lokacin yana  mataimakin  kakakin  majalisa.mukaje  mu biyu.muka  fada  masa  bukatunmu.yace  muna da  inda muke niyyar kamawa.nace  gidan  rabe  kaita  mai taya.ginin ya kallon ofis dina. Bilya yayi  hanya aka kama mana na shekara  daya.wannan  dauke  taro  da nayi  sila  daga gidan rediyo  zuwa  ofis  din  NUJ  da aka  kama  na daga  laifin  farko  da nyi ma wasu yan gidan  rediyo.

 

Da  yake  ofis din  yana  kusa da  nawa. Duk taron  da  za ai  said an huta ofis nawa  kafin a  hau sama  wajen taro.sai  ya zama ko  misali  za aid a ofis  din  NUJ  sai  ace yana kallon ofis na  VC. Hutawa  da  yadda  zango a  ofis nawa,dai  dai daya ne daga  cikin masu  jagorantar  NUJ   a  kasar  nan  ba suyi  ba.in aiki  ya  kawo su, musamman  lokacin  kamfen na  kungiyar  nasa. In sunzo  Katsina  neman  goyon baya.

 

Wani  lokaci  anan  ake  zama  kafin a hau  saman bene inda ofis din yake,wani  lokaci   a tsaya  nan ma  ayi.  Taron. Wannan  na daga cikin  laifufukan da na yi  ma wasu, aka ce na  maida  ofis din NUJ  ofis  nawa.

 

Duk nasarorin  da muka  samu.a  lokacin   da muna  jaragoncin ya  samu ne  sakamakon  aminci  da  yarda  da juna  dake tsakaninmu.IZMA  ya   san  cewa  idan  har ya  mika man amana  ko  wani  aiki  sai zan yi   shi  tsakani  da Allah. Wannan ya sanya wani hadin kai  tsakanimu.

 

Wanda  hatta wasu  shugabannin kungiyar na  wajen jihar  Katsina.sun  fahimci wannan  kuma  suna jinjina mana akan  haka. Misali  zainab  rabo  ringim shugabar  kungiyar  mata yan jarida ta wannan  shiyya ta  fada  cewa  bata  taba ganin   masu  hadin  kai   kamarmu  ba. Shugaban  NUJ na  jihar  Kaduna  ma ya  fadi  haka.haka   mataimakin  shugaba na kasa na NUJ Nawannan shiyyar, da  sakatarensa shehu, sun fadi. Haka.  Wannan hadin kai  na daga  cikin laifin  da  akai ma wasu.wai  an mallake izma kullum yana  ofis nawa  sai  kuma  yadda  nace masa.

See also  Tarihin Marigayi Khalifa Isyaka Rabi'u

 

Matsalar   bas  wadda   shugaban  kwastam na kasa ya  bada.anyi  tarurruka  sau ar ba in  da shidda  akan wannan  KES.duk  ba  wanda ban halarta, ba  wanda  banda  rubutaccen me ya  faru  da rawar  da kowa ya taka.ni  na sa  hannu  a  madadin  NUJ   a rubutacciyar  takardar  da   aka sulhunta  maganar  a gidan  Dakta  sani  lugga  wazirin Katsina.daga  bangarensu  kuma  mutum biyu  suka sanya  Hannu.

 

Ni   na  sanya  Hannu a  madadin  NUJ   a  wajen yan sanda  cewa  , an  janye  maganar. Bas  din  da yanzu  ita  kungiyar  ke takama da ita.kuma  ya yan  kungiyar ke  amfana.wanda  ana  bada ita  aro ga duk dan kungiya  day a  bukata.bas  na amfanan kowa.amma  bakin  jinin  bas  a kaina ta. dawo.laifin da akaima  wasu me yasa  aka amso bas.? Wasu  kuma me yasa zan bada   direban  dake kula  da  bas?  Me kuma yasa  izma ya bada  umurnin  duk mai son aron bas  ya zo waje na? ya  kawo  takardar  bukatar   haka?

 

Mun  kawo  karatun  IIJ  a   Katsina. Dani  akaje  Abuja. Aka zauna day an makarantar  a  Katsina.da  za  a fara  karatun,sakatare  wanda a lokacin  yana  jarabawa  a wata  makaranta  da yake.sai ya  damka  duk al amarin makarntar  a wajena.a  ofins dina aka ruka rijista.duk  abinda  ya shafi makarantar   har zuwa  fara  karatunsu.yaran  ofis dina  suka  rika  tafiyar  da  lamarin.wannan  na daga cikin  laifin da akai ma wasu  me yasa haka?karatunma  ya  kwace?

 

Duk  tsawon  lokacin  da Aminu  ahamad ayek shugabantar  kungiyar  NUJ ba a karbar  kudin kungiya  daga  maiaikatan. Watau  ba a cirewa  daga labashi. Lokacin  tsarin  mulkin kungiyar ya  soke a rika amsar  wadannan kudade. Sai dai  duk shekarra a  rika  biyan kudi  ga uwarkungiya.da  aka  canza  tsarin  mulkin cewa  a rika  cire  kudin daga albashi.

 

A  Katsina  a kwai  kafofin watsa  labarai  kamarsu.ma aikatar  watsa  labarai.gidan  rediyo  da talabijin wadanda  ma aikatan jaha,ana  canza  wancan  tsarin, aka fara cire  masu.nan kuma wata muhawara  ta tashi. Akan yadda  za arika  raba kudin.kamar yadda tsarin  mulki ya tsara.

 

Anyi  ta zama.wanda  daga  baya  aka yanke shawarar  a rika ba wadanda  ake cire  kudaden nasu wani  kaso.aka  sanya  waje na  za a rika  zuwa ana amsar wannan kason.ni za azo  la rubuta  takarda  I n baka kamar yadda  aka  ce.subhannallah. wannan  shima ya tayar da wata muhawarar.?ya  za ai wanda  shi ba a cire masa kudi,ya rika  bamu  kudi.?wannan aikin   ma ajin  jam iyya ne?

 

Daya  daga  cikin  nasarar  da muka samu itace.samarwa  da kungiyar  waje na din din.wanda  aka bamu  tsohuwar  ginin  KTTV  da kuma NTA lokacin  da aka bamu. An ta  samun asakala  tsakaninmu da  hukumar  Nta.wata  rana   IZMA ya  same ni  yace  y azamu iya amsar  ginin nan ya dawo wajenmu  dari bisa  dari?

 

Saboda   duk lokacin da yayi  ma Nta  Magana. Sai  su bashi  wani  labari  daban.muka tsara  cewa  a farfado da kaddamar da kwamitin dattawan kungiyar.a kuma  ginin   IZMA  yace  ya  bar  man  aikin  akai  Magana da sakatare  shima ya  goyi  baya.

 

Na  tsara yadda  za a amshi ginin a  matakai uku.lalama biyu  rikici  hawa  na karshe.an amshi ginin amma yadda  aka bi  har  sai  da  shugabar  Nta  ta  jahar  wadda  mutum niyar kirkice  kuma muna mutumci  da ita.ta  bugo man  waya tana nuna  man  rashin  jin dadinta akan wasu abubuwa da akace  sun  faru,wadanda  duk karya ne. wasu ne  a NTA  din  da suke  jin  cewa kamar  ginin zai  subuce hannunsu,suka  kirkira, nan ma na san nayi wasu   wadanda  akai ma  laifi.ana amsar ginin aka nemi wa zai  zauna ya kula da wajen? Kyauta tunda  NUJ bata da kudin daukar  nauyin wani, nace  ina yaran  da zan tura.na tura su,wannan ma an ma wasu laifi.

 

A Tsawon shekaru  uku nan  da watanni.na  zama kamar  wani  garuje.duk  wasu  abubuwa  sai  ace ni.sauran  sun rika taka tsan tsan,ni kuma duk abin  day a zo  yadda  ake son sahaka  za ayi. Kodazai batawa  wasu rai.ba ruwa na.

 

Hakika  wata  rana  dana  ya taba  jawo  hankalina.yace  baba na  kanzo nan  ofis ina zama ina  lura dayyda  kake tafiyar   da  lamurranka.yace  gaskiya kana kuskure  akan yadda kake tafiyar  da  harkar  NUJ.ka tara komai  akanka. Aikin  ciyaman kaine.skatare kaine . ma aji  kaine.mai  binciken kudi kaine,mai bicike da tan tancewa  kaine.

 

Yace  baba  ka saba ma duk wata  kaida  da  kake koya mana  a yadda mutum  zai kauce ma  sabun  sabani da  ajama  a. idan yana  shugabanci.yace  na lissafa  na lissafa naga ba inda  zaka iya  fitar  da  kanka  daga  halin daka sa  kanka.sai  dai in har ba zaka sake  neman tsayawa takara ba.amma in fada maka gaskiya  har naji  duk na  tsani wannan matsayin da kake ciki.saboda  sakamakonsa bai da kyau  a iya hange na,

 

Wannan  damuwa ta Muhammad  wanda  dalibi ne  wata  Babbar makaranta  ana Katsina. Har  sai  da  ya fada ma  mahaifiya ta  da yai man tambayar na   zayyana  masa daki daki cewa. Ga yadda na samu kaina  har duk wannan  abubuwa suka  faru.na ce  nima na yanke shawarar  ba sake  tsayawa takara.wannan   matsaya ta faranta masa rai  sosai, ya  kuma ce  wannan ya cire masa damuwar dake damunsa.

 

Nayi tasiri  sosai  a  tsakanin yan kungiyar NUJ.amma  a waje, ko cikin dangina wasu basu san matsayin da nake rike  dashi ba.balle jami an gwamnati. Balle  sauran  yan cikin  gari, kowa ina mua amala dashi ne a  matsayin sunan  da ya sanni, a kuma yadda ya sanni.

 

Ban taba amfani  da matsayi nab a na nemar kaina  wata alfarma. A duk Katsina.ba abinda  zan nema ya gagare ni da  matsayin da nake.akan haka na natsu bani bukatar  sake tsayawa takara.

 

KASHI,NA UKKU YADDA NA SHIGA  ZABE NA KUMA SHA KAYE..

 

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here