Jarumar Finafinan Hausa Hauwa Maina Ta Rasu

0

Shahararriyar jarumar nan ta fina-finan Hausa Hajiya Hauwa Maina ta rasu jiya Laraba da daddare.

Rahotanni sun bayyana cewa ta rasu ne a asibitin Malam Aminu Kano bayan ta sha fama da jinya.

Ana sa ran za a yi jana’izarta a  yau Alhamis a garin Kaduna, inda take zaune gabanin rasuwarta.

Hauwa Maina na daga cikin matan da suka jima suna fitowa a fina-finan Hausa.

Tun 1999 ta fara fim din Hausa, bayan ta koma garin Kaduna da zama.

See also  FG hands over 1000 housing units, food and non food items to Borno state government.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here