Majalisar Dinkin Duniya tayi Allah wadarai da kisan Hauwa Liman
Daga Zubairu Muhammad
Sakatare Janaral na Majalisar Dinkin Duniya Mr. Antonio Guterres yace Majalisar Dinkin Duniya ta nuna damuwa da wanan kisan rashin imani da Kungiyar ta’addaci ta Boko haram tayiwa ma’aikaciyar jin kai a bangaren kiwon Lafiya ta (ICRC) dake gudanar da ayyuka a Arewa maso gabashin Nijeriya.
Da take Magana a madadin cibiyar yada labarai na Majalisar Dinkin Duniya Hajiya Safeeya Muhammad tace, Majalisar Dinkin Duniya ta nuna damuwa dangane da kisan gillar.
Tace ; Sakataren ya nuna damuwa inda ya kara da
Yace; Hauwa Muhammad Liman ta kasance ma
tausayawa ga wadanda suka fada cikin wanan bala’i da suka rasa matsugunansu da suka shiga kuncin rayuwa. Saboda haka ne ta bada lokacinta take gudanar da ayyukan jinkai baji ba gani.
Yace; Kungiyar Boko Haram sun kama Hauwa Muhammad Liman ne tun cikin watan uku mai makon su saketa amma sukaci gaba da riketa daga bisani cikin wanan makon sukayi mata kisan gilla .
Sakataren Majalisar Dinkin Duniya Mr Antonio Guterres yace Majalisar Dinkin Duniya tana jajantawa iyayen wanan jaruman dakuma kungiyar bada agaji a vangaren kiwon Lafiya ta (ICRC) yace; babu wanda zaiji wanan abinda ya faru da Hauwa Muhammad Liman yace; hankalinsa bai tashi ba. Ya kara da cewa
Bai kamata arika kashe masu bayar da agaji ba kosuwaye.
Sanan yayi roko ga masu fada aji dasu karfafa giwa ga masu bada ayyukan jin kai saboda su samu kwarin giwa gudanar da ayyukansu. Ya kumace masu ayyukan jinkai ko na ceto suna taimakawa miiyoyin alumma ne da rikicin Boko haram ya hanasu zama a gidajensu dake Arewa maso gabashin Nijeriya.
Sakataren ya kara jajantawa miiyoyin alumman Nijeriya da ambaliyan ruwa ya rutsa da gidajensu, wanda yayi sana diyar mutuwar mutani sama da 200 kuma 1.300 suka samu manyan raunuka