Wa Ya Zagi Ahmad?

0

Kwanakin   baya  muka  hadu   a   Kaduna  don  murnar  cikar    farfesa  Ibrahim malumfashi   shekaru   a  duniya.kafin nan  na bi  wani  rubutun da  ya rika  yi, na  cikarsa  wadan nan shekaru  a filinsa  da  ke jaridar   AMINIYA.rubutun  ya  burge ni  yadda  ya tuna baya.  Wannan yasa  na tuno  da wani rubutun  tuna  baya.  Dana buga  a   mujallar Matasa.wadda  ta fito  a  shekarar  2009.Na  ga yakama ta   in sake  buga  shi  ba   canji  a  filin HANTSI   don makaranta na  su  dan   dara.

Musammam  wancan  da  aka  buga   sai   da  dan kincimi ya  neme ni  y ace  ai na  rage   labarin  a wani  waje  a  labarin  don kuwa  ai  said a na…………….. NI  kuma  nace ai wannan  sirri  ne.  a sha  karatu  lafia    amma  don Allah   kar kai  man  dariya.

Kakannimu da muka tashi a wajensu  sun horas damu  zumunci,wanda mukan je gaida dangi kowa ce  jumma a.kullum aka gama salla  zamu rako kakanmu gida tare  da sauran jama a.daga nan zamu ci abinci rana ,sannan sai mu shiga gari gaida yan uwa da abokan arziki.

An saba da sanin gaida dangi da yaran da aka ba tarbiya irin  wannan kanzo  don haka zaka ga dangi kana aje kudi wadanda akan raba ma yan ziyarar jumma a.wasu kuma kana je kayan malaki ne wanda suke ba yaran ,yan uwa kanyi amfani da wannan dama su gargradi yada su kara kara kokari a wajen karatunsu.su kan kuma amfani da ziyarar wajen yi masu nasihohi akan rayuwa  da nasararta.

Da yake dangin nawa yawa garesu,ni da wasu abokaina su muntari na kan barya muka raba ziyarar dangin namu  zuwa gida  biyu,yau in munje wani sashen wani lokaci kuma sai muje wani barayin,

Mukan farad a unguwar sagi, wadda  ke cikin  birni wanda yanzu  a akai  kasuwar   cake  a  kusa da anguwar.sai mu fada bakin gida sai kuma mu shigo ta marnar kadabo mu rankaya zuwa marnar tafki,mu bi ta filin bugu mu ratsa chake mu isa sararin tsako. Mushogo longuna mu  je kasuwa muna takawa dai daya  domin  akwai tsaba aljifunan mu.muna iya sayen duk wani kayan dadi d muke sha a wa.wani satin kuma sai mu bi ta wani layin.

Wata juma a bayan mun raka mallam gida[kakanmu]na nemi mai kan tabarya[bad nickname na muntari]

Ban ganshi ba.sai kawai na fito yawo na ni daya, wannan satin zanbi ta kofar soro ne in bi layin  unguwannin dake wannan zagayen ,na taho har bakin kofar soro  a filin na kofar soro sai na gawani mai wasa da maciji,na ko tsaya kallo,yayi ta abubuwan jan hankali kuma masu  ban mamaki daga can sai ya koma tallar magani,yana tallar wani magani wais hi”” ki bugu,””wata lay ace zaka saya  zaka je a  dinke maka ita,mai maganin yace in kana tare da layar  kowa yazo bugunka hannunshi zai sage har  sai kayi masa mari  goma ko kuma ya lashi takashinka.

Nan da nan sai naji ina da bukatar sayen wannan laya,ba kudi aljifuna ai sai na ruga  gidajen zumunci da zanyi na shiga ta kofar  soro na fado saulawa na biyo tab akin asibiti  na zo galadunci .na dawo wurin mai saida maganin “”ki bugu””duk inda gidan dangin da aka nemi a tsaida ni hira  ko kuma wata nasiha sai ince sauri nake ayi man hakuri sai wani sati in na dawo,

Na iske mai magani ya tashi yana ta saurin hada kayansa na mika masa kudi na amshi laya daya yayi mani bayanin daki yadda zanyi da ita.na karba na kama hanyar gida ina ji na da wani sabon karfi.dama inajin kamar duk an raina ni saboda duk cikin abokaina nine dan karami acikinsu.’’zan nuna masu ni kodagone a ganka a raina ataka ka karya mutun’’ina fadi azuciya ta,

Ina kuma tafiya ina tsara ya zangwada  wannan karfin iko nawa yadda kowa zai sani kuma a shiga taitayi?in saka wannan in kwance in tsara wancan in warware,abokaina kowa na dauko sai inga ba wani dalilin fada dashi.

A gabashin  unguwarmu akwai wani tafki da ake kira lahirar makafi saboda raminsa da kuma girmansa,a kusa da wurin akwai wani mai saida dafaffun kanu, a gidan wasu yan damben gargajiya na sauka,a cikin yan damben akwai wani da ake kira Iro dan kincimi.

See also  AYAR ALLAH A KOFAR DURBI KATSINA

Shi iro dankincimi kowa  ya sanshi  a yankin saboda  yana yawan kashe mutane  a dambe.amma a mu amala ba ruwanshi da kowa mutumin kirki ne,a siffa kuwa abin tsoro ne, domin kuwa gashi gajere.dirarre.kuma kakkarfa,kuma baki ne wulik. Mutumin wani gari mai suna doso a jamhuriyar nijar.

Zuciya  ta sai kawai nayi shawarar cewa  in har  nayi fada da dan  kincimi a gaban jama a  lallai zan kira lamba.don haka sai kawai naje na tsokani dan kincimi cikin tsokanar hard a dangwalar masa hanci  har kuwa  na  fusata  shi,har y ace in fadi ina nakejin zamu iya haduwa a kara?na wani Harare shin a ce mu  hadu dandalin wasanni dake wajen gidan waya bayan anyi  isha I,

A yankin baki daya nan yara tsarrakinmu ke haduwa suyi wasa . akwai wani katon fili.zakaga yara  gungu gungu  suna wasanni kala kala,irinsu tahole da bida da was an burum akanyi kuma wasa mai suna  ya zagi Ahmad,was an shi ya zagi Ahmad wani wasa ne wanda kowa kan cire  rigarsa, duk wanda yayi kure acikin was an sai a bishi da dukaana cewa ya zagi Ahmad har ya ruga ya kai wani wuri ya  duka yana ya tuba,.kila wata rana in rubuto irin wasannin  da akeyi a wannan fili da salonsu.

Na zabi wannan filine, saboda a lokaci guda  akan iya samun yara masu yawa suna wasa kala kala . A nawa zabin  idan na sagar da hannun dan kincimi  a wannan fili kowa zaiji labara  kuma zan zama gwarzo, kowa zai rika jin tsoro na.

Gab da magariba  Dan kincimi yazo har kofar  gidanmu yana  neman jin ko abin da takule shi dazun da wasa na keyi sai kawai na rika wani cin magani nace  mu hadu kawai  a  dandali in an jima, yana gidanmu har aka kira sallar  magriba  ya shiga masallacin gidanmu ya yi salla ni kuma na dai daita sahu kusa dashi na taka masa dan yatsa don dai in kara hassalashi,

Tun wuri na isa fili, da laya ta matse  a kubakar wando,ga wasa nan anayi hululu kala kala,sai sowa daraha kake ji iri iri,ni kuma ina tunanin cewa nan da wani lokaci zan  zama kamar wani sarki  a tsakanin yara,zan juya su in sarrafasu sai yadda nayi dasu,zan taka in murje tunda ina da karfi,can sai naji tafiya bayana

Ina juyawa sai naga ashe dan kincimi yake isowa inda nake,kafin ya karasa isowa saina fara tsalle  irin yan damben turawa [boxing]yana isowa sai na debo kasa na nuna masa nace gata tsiya gata arziki ya kabe daya  sai  ya  falle tatsiyar. Sai naja baya  nashafi  layata na nufo shi,zan kai masa bugu da niyyar in ya maido bugun sai hannunsa ya sage  shikena abin nema ya samu,

Dan kincimi  sai ya cabe hannayen gudaa biyu ya hada su wuri daya ya rike   ya danna su kasa ya sa hannunsa  guda yayi ta falla mani mari  nan na rika ganin wasu irin taurari,san nan  narikia jin wani  kida maras dadi a kunne na,

Da kyar na kubce,na juya da gudun tsiya,ina gudu sai na fada cikin masau was an way a zagi Ahmad?dai dai lokacin da na shiga an fara bugun wani,sai kawai sukayi tsammanin cikinsu nake sai ji kake tas tas bugu kota ina,nan na kara rudewa na daka da gudun tsiya,su kuma suka ce dawa aka hada mu bada kai ba!

Bugu ko ta ina da haka na kai gidan kakata na fada dakin tan a shige kuryar dakin na kuma sige  kuryar gado na yi lamo.kakata ta kalleni tace daga ina  nace daga sama.aka jefo ni,Allah  jikanta ]ta nufi waje  ta iske yan wasa kowa da rigarsa a hannu yana jiran in fito yasha moro ga dankincimi  tsaye yana haki.

Tace ya akayi suka ce  Ai iya shine  ya zagi Ahmad ,tace to kuyi hakuri suka juya  suka tafi  tana komowa daki ta daga karkashin gado ta ganni duk a rude iadanu na wuri wuri. Tace sunce  wai kaine ka zagi Ahmad?nace  cikin tsoro da firgici  kwarai kuwa har ma na dangwaran masa hanci!na taka kafarsa na murza!iya tace to maganinka kenan !gobe  ma ka kuma!

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here