Yadda Ruwa Da Kankara Ya Lalata Sama Da Gonaki 300 A Jahar Katsina

0

Wata gagarumar ruwan kankara ya lalata gonaki da gidajen jama’a a yankunan Dutsen-Kura/Kanya da Gozaki a karamar hukumar Kafur ta jihar Katsina.

 

Malam Abdullahi Gozaki, wani mazaunin garin Gozaki ya sanar da Daily Trust cewa babu wani mutum daya da ya taba fuskantar irin wannan lamarin a yankin

 

Yace gonakinsu, rufin gidaje da gilasan motoci duk suna lalace sakamakon ruwan kankarar da aka yi na tsawon mintuna

 

Ya jero yankunan da lamarin ya shafa kamar haka: Gidan Danwada, Gidan Sabo, Kabalawa, Unguwar Tsamiya, Dandabo, Unguwar Maigarma, Uguwar Wanzamai da Unguwar Fulani

 

A yayin tsokaci kan faruwar lamarin, shugaban karamar hukumar Kafur, Alhaji garba Kanya, yace kankarar ta lalata sama da gonaki 300 a yankuna da dama

See also  BUHARI'S ROADS INFRASTRUCTURE IN ABUJA WAXING ON!

 

Ya kara da cewa, hukumomin da suka dace daga ciki akwai Hukumar kula da aikin noma da raya karkara, KTARDA da hukumar kula da tallafiin gaggawa, SEMA, duk an sanar da su yawan barnar

 

majiya: legit hausa . . . . .  legit hausa

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here